Site icon Arewa Voice

Tarihin Rayuwar Kwankwaso & Tarihin Siyasar Sa

Tarihin Rayuwar Kwankwaso & Tarihin Siyasar Sa

Tarihin Rayuwar Kwankwaso & Tarihin Siyasar Sa

Doctor Rabiu Musa Kwankwaso shahararren ɗan siyasa ne kuma tsohon ɗan takarar shugaban kasa a shekarar 2023, a Nigeria kuma tsohon sanata, wanda mabiyansa ke masa lakabi da “Kwankwasiyya”.

Tarihin Rabiu Musa Kwankwaso

An haifi sa ne a ranar 21 ga watan Oktoba, cikin shekarar alif 1956, a kauyen Kwankwaso da ke karamar hukumar Madobi na jihar Kano dake arewa maso yammacin Nigeria.

 

Kwankwaso ya taba zama Gwamnan Jihar Kano daga shekarar 1999 zuwa shekarar 2003. Amma a zaben shekarar 2003 ya fadi zabe wanda ya hana shi komawa ofis nasa na gwamna, amma daga baya tsohon Shugaban kasa Nigeria Olusegun Obasanjo ya nada shi Ministan Tsaro a wancan lokacin. 

 

Sa’annan an sake zaban shi a matsayin Gwamnan Jihar Kano a zaben shekarar 2011. Inda ya yi mulki daga shekarar 2011 zuwa 2015. Bisa ga ranar haihuwarsa, idan aka duba Kwankwaso a halin yanzu yana da shekaru 66 kuma zai cika shekaru 67 a duniya nan da ɗan wasu watanni.

 

Bayanan Kwankwaso:

 

ASALIN SUNA: Rabi’u Musa

SHEKARU: 67

SUNAN BABA: Musa

SUNAN MAMA:

matakin karatu: Digiri

asalin jiha: Kano

KASA: Nigeria

MATA: Salamatu (1)

YARA: Shida (6)

SANA’A: Siyasa, Kasuwanci

Twitter: @KwankwasoRM

Instagram: kwankwasorm

 

Tarihin Siyasar Kwankwaso

Kwankwaso da ganduje

Tarihin farawar siyasar Kwankwaso ta faro ne tun shekarar alif 1992, lokacin da aka zabe shi a matsayin dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar tarayya ta Madobi,  zaben da aka yi masa a matsayin mataimakin kakakin majalisa a majalisar a wancan lokaci ya jawo masa budin ƙwaƙwalwa a siyasan ce (experience). Musa Kwankwaso a lokacin ya kasance dan jam’iyyar  SDP ne, wanda yake a karkashin jagorancin marigayi tsohon shugaban kasar Najeriya wato  Shehu MusaYar’adua.  

 

A zaben shekarar alif 1999 Rabi’u Musa Kwankwaso ya tsaya takara, inda kuma har ya lashe zaben gwamnan jihar Kano a karkashin jam’iyyar PDP. Sa’annan a shekarar 2003 ya sake tsayawa takara karo na biyu amma bai samu nasara ba.

A lokacin taron tsarin mulki na Cikin shekarar alif 1995, an zabi Kwankwaso a matsayin wakili daga Kano, a matsayin dan jam’iyyar People’s Democratic Movement karkashin jagorancin Yar’adua.

 

Bayan da Kwankwaso ya sha kaye a zaben shekarar 2003, tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya nada shi ministan tsaro. An sake zaban shi a matsayin gwamna a karo na biyu a shekarar 2011. Inda ya yi mulki har zuwa shekarar 2015.

 

 Rabi’u Musa Kwankwaso bayan karasa wa’adin mulkin sa na biyu a shekarar 2015. Ya sake sayawa takara, amma a wannan karo a matsayin ɗan takarar Sanata ne ya saya, kuma Allah ya bashi nasara aka ya lashe zabe a matsayin Sanata mai wakiltar Kano ta tsakiya a karkashin jam’iyyar APC.

 

 A shekarar 2018, Dr Rabi’u Musa Kwankwaso ya sauya sheka zuwa karkashin jam’iyyar PDP inda ya tsaya takarar shugaban kasa a zaben fidda gwani, inda anan ma ya sha kayi, abokin hamayyar sa wato Atiku Abubakar shi ne ya lashe zaben, inda daga baya shi ma ya sha kayi a babban zabe.

Jerin Jihohin Arewa 

Kwankwaso ya ci gaba da zama a karkashin jam’iyyar PDP har zuwa ranar 30 ga watan Mayu, inda ya koma jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), bayan komawarsa ya sanar wa jama’a aniyar sa na sayawa takara.

Inda a ranar 8 ga watan Yuni, Kwankwaso ya fito a matsayin dan takarar shugaban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar NNPP a zaben shekarar 2023.

 

A zaben shekarar 2023, da Alhaji Bola Ahmed Tinubu ya lashe, Musa Kwankwaso ya yi nasarar zuwa na hudu bayan Atiku Abubakar ɗan takara daga jam’iyyar PDP, wanda ya zo na biyu. Da Peter obi ɗan takarar daga jam’iyyar Labour Party (LP), shi kuma na uku. Bola Ahmed Tinubu na farko daga jam’iyyar APC.

Sanatoci mafi dadewa a tarihin Nigeria

Aure Da Iyalin Kwankwaso

Dr Rabi’u Musa Kwankwaso ya aure ne a shekarar 2000 inda ya auri matarsa mai suna, ​​Salamatu Rabiu Musa, kuma Allah ya albarka ce su da ya’ya shida (6). Sai dai kuma wasu daga cikin jama’a na ganin cewa Kwankwaso bai yi aure da wuri ba, wanda hakan kuma na iya zama gaskiya.

Ilimi/Karatun Kwankwaso

Rabi’u Musa Kwankwaso ya halarci makarantar firamare ne a garin Kwankwaso, Gwarzo Boarding Senior Primary School, Wudil Craft School da Kano ta Technical College.

Sa’annan ya wuce jihar Kaduna inda ya shiga makarantar Polytechnic inda ya yi karatun sa na Diploma na kasa da na kasa. Kwankwaso a lokacin ya kasance shugaban dalibai mai himma a lokacin da yake makaranta kuma ya kasance zababben jami’in kungiyar dalibai na jihar Kano gaba daya.

Kwankwaso ya kuma tafi kasar England inda ya halarci jami’ar karatun digiri na biyu a Burtaniya daga shekarar alif 1982 zuwa shekarar 6 1983 a Middlesex Polytechnic. Ya kuma halarci Jami’ar Fasaha ta Loughborough inda ya sami digiri nasa na biyu a fannin injiniyan ruwa a shekarar alif 1985.

Tarihin Peter obi

Mahaifin Kwankwaso

Baban Dr Rabi’u Musa Kwankwaso mahaifinsa shi ne hakimin kauyen garin Kwankwaso mai lakabin Sarkin Fulani a wancan lokacin. Daga baya an kara masa girma zuwa Hakimin Madobi, sa’anan aka sake kara masa mukamin Majidadin jihar Kano, daga Majalisar Masarautar jihar Kano ta Sarki Ado Bayero.

 

Ayyukan Ci Gaba Da Kwankwaso Yayi

Ga jerin ayyukan da Dr Rabi’u Musa Kwankwaso Yayi a lokacin da yake ofishi:

 

 

 Muƙaman Da Kwankwaso Ya Rike

Darajar Dukiyar Kwankwaso

Dr Rabiu Musa Kwankwaso yana daya daga cikin shahararrun manyan ‘yan siyasar Najeriya. An kiyasta darajarsa dukiyar Kwankwaso inda ta kai sama da dala miliyan $14.

Kuma a jihar Kano shi ne wanda ya fi kowane ɗan siyasa kuɗi da dukiya a jihar Kano, kuma shi ne wanda ya fi kowane mutum a jihar Kano farin jini a wajen al’umma. Mabiyansa na masa lakabi da “Kwankwasiyya” amana.

Jerin manyan jihohin arewa

 

Exit mobile version